Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kama wasu ‘yan sanda 14 na bogi da suka kai farmaki gidan mai shari’a Mary Odili a ranar 29 ga watan Oktoba.
An ce jami’an jabun sun kasance ne karkashin jagorancin babban Sufeton ‘yan sanda (CSP), Lawrence Ajojo, wanda Kuma ya amsa laifin sa na cewa, shi ba jami’in rundunar Yan sanda bane.
Da yake baje Kolin wadanda ake zargin, a ranar Alhamis a sashin binciken manyan laifuka na rundunar dake Garki Abuja, kakakin rundunar, Frank Mba, ya ce wadanda ake zargi da aikata laifin sun fito ne daga sashin daban-daban.
A wata hira da manema labarai yayin baje kulin, CSP na karya, Ajojo ya yarda cewa “shi ba jami’in ‘yan sandan Najeriya bane.”
Comments 1