Wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, sun sace wani mutumi mai suna Adamu Garba Ali, mai kimanin shekaru 35 da ke zaune a Anguwar Dogo Nini layin Lamba Idriss ward Potiskum jihar Yobe. Lokacin da wakilinmu ya isa wajen da abin ya faru ya samu zantawa da daya daga cikin iyalan nashi kuma ya labarta masa duk abinda ya faru. “Shi dai Garba Adamu kani yake a wajen mahaifina, kuma ya fita daga gida ne da misalin karfe goma na safe ranar juma’a to sai kuma wani lokaci zuwa karfe 8:30 na dare sai labari ya riske mu ga abinda ya ke faruwa da shi kuma an kira wayan shi bata shiga. “ “A daidai wannan lokacin sai muka dunguma zuwa Ofishin jami’an tsaron ‘yan Sanda dake garin Potiskum muka sanar da su duk abinda yake faruwa,kuma muka wuce Ofishin Cibil Defends suma muka fada musu halin da ake ciki. “ “Bayan mun je an dauki bayananmu din mu muka kara garzayowa zuwa Asibitocin garin Potiskum domin duba sa ko yana nan, saboda wani lokaci za a iya yin hatsari ba a sani ba. To nan ma dai bamu yi dace ba, saboda bamu same sa ba a wajen. “ “Muka dawo gida muka bar wa Allah komai, kuma muka ci gaba da addu’ar Allah ya bayyanasa, to muna nan dai sai da misalin karfe 2 :30 na dare kanina ya kira shi muka yi sa’a wayar ta shiga amma kuma bai dauka ba, muka tura masa sako yana ina? sai ya kira mu a waya ya fada mana cewa zuwa yanzu ba zai iya gane wajen da yake ba kuma yana tsammanin zuwa anjima za a karbe wayoyin da suke hannun su. “ “A wannan lokacin da yake mana magana muna gashin cewa kamar ba shi kadai aka kama ba, saboda yana ce mana za su karbe wayan su. “ “Lokacin da muke magana da shi ya fada mana cewa yana dawowa ne daga banki wajen ciro kudi shi ne hakan ta faru da shi, amma kuma bai fada mini takamaimen su wanene suka kama shi ba kawai shi dai bai san inda yake ba “. “To har zuwa yanzu da nake magana da kai bamu san inda yake ba kuma bamu samu wani labari ba, wayar sama yanzu ta daina shiga duk da yake mun sanar da hukuma halin da ake ciki kuma sun ce za suyi iya bakin kokarin su. “ Har zuwa lokacin hada wannan rahoton rundunar ‘yan Sandan Potiskum basu tabbatar da faruwar lamarin ba, kuma duk kokarin da wakilinmu ya yi domin ji ta bakinsu bai yi nasara ba.