Akalla mutum 29 kawo yanzu aka tabbatar da sun mutu a wasu tagwayen hare-haren ta’addanci da mayaka masu ikirarin jihadi suka kai yankin arewacin kasar Burkina Faso a yammacin ranar Lahadi.
Sanarwar da fadar gwamnatin kasar ta fitar a yau, ta nuna cewa mayakan sun dasa bom a jikin wata motar dakon kaya da mutane a yankin Barsalogho inda kuma nan ta ke ta kashe mutane 15.
Acewar sanarwar mai dauke da sa hannun kakakin fadar shugaban kasar Burkina Faso Remis Filgance Dandjinou galibin wadanda suka rasa rayukansu ‘yan kasuwa ne dake kan hanyar dawowa daga safara.
Ka zalika sanarwar ta bayyana hari na biyu a yanki mai tazarar kilomita 50 daga inda mayakan suka kaddamar da na farko, inda a nan kuma suka bude wuta kan mutane 14 wadanda suma nan take suka rasa rayukansu.
Wata majiya ta bayyana cewa dukkanin mutane 14 da suka rasa rayukansu a harin na biyu, direbobin motocin da ke safarar abinci zuwa yankin da aka tsugunar da ‘yan gudun hijira ne.