Tawagar jami’an tsaron hadin gwiwa a Ekiti ta kashe wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne a wurin karbar kudin fansa a wani dajin da ke tsakanin iyakar jihohin Ekiti da Kwara.
Wata majiya ta shaida wa manema labarai a Ado Ekiti cewa, hadin gwiwar sojoji da ‘yan sanda da kuma jami’an tsaro na yankin da ake kira Yan Banga, ne suka hallaka mutumin, Adamu Abashe, sun kashe shi a cikin wani dajin da ke Eruku a jihar Kwara.
Rushewar Gini: Gwamnatin jihar Legas Ta Ayyana zaman Makoki na kwana 3
Zamfara: Ƴan sanda sun Kubutar da wasu mutane da aka yi garkuwa da su
An ce jami’an tsaron sun yi wa ‘yan fashin kwanton bauna ne a daidai lokacin da aka biya kudin fansa naira miliyan 2.1 ga wadanda aka sace, inda suka bi su bayan sun karbi kudin har sai da suka harbe wanda ake zargin.
Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan Ekiti, Sunday Abutu, ya gabatar da gawar mai garkuwa da mutanen a hedikwatar ‘yan sanda da ke Ado Ekiti a jiya Alhamis.
Comments 1