Akalla ‘yan jarida 62 ne aka kashe saboda yin ayyukansu a shekarar 2020, a cewar Hukumar Kula da Ilimi, Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO).
Hukumar ta Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa tsakanin shekarar 2006 zuwa 2020, kwararru sama da 1,200 ne suka rasa rayukansu kamar haka kuma tara daga cikin goma, wadanda suka yi kisan ba a hukunta su ba.
A shekarar 2021, saboda kididdigar irin wadannan, ranar Duniya domin Kawo Karshen Hukuncin Laifukan da ake Yi wa ‘Yan Jarida, na nuna muhimmiyar rawar da ake takawa wajen gabatar da kara a gaban kotu, ba wai kawai wajen gurfanar da masu kisan kai a gaban kotu ba, har ma da hukunta masu barazanar tashin hankali.
A cikin sakonsa a ranar Talata, Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres, ya yi nuni da cewa, ‘yan jarida da dama sun rasa rayukansu a yayin da suke yada rahotanni, amma yawan ma’aikatan yada labaran da ake kashewa a wajen wuraren da ake rikici, ya karu a ‘yan shekarun nan.
“A kasashe da dama, kawai binciken cin hanci da rashawa, fataucin mutane, take hakkin dan adam ko kuma batutuwan da suka shafi muhalli na jefa rayuwar ‘yan jarida cikin hadari,” in ji shugaban na Majalisar Dinkin Duniya.
Laifukan da ake yi wa ‘yan jarida na da matukar tasiri ga al’umma baki daya, domin suna hana mutane yanke shawara mai kyau.
’Yan jarida na fuskantar barazana mara adadi, kama daga sace-sace, azabtarwa da tsarewa ba bisa ka’ida ba, zuwa kamfen na ɓarna da cin zarafi, musamman a fannin kafafen yada labaran zamani.
Ga Guterres, “laifukan da ake yi wa ‘yan jarida na da matukar tasiri ga al’umma baki daya, saboda suna hana mutane yanke shawara.”