Daga Abdullahi Kebbi
Rundunar ‘yan sanda jihar Filota ta bayyana cewa an kashe mutum 5 tare da kona gidaje 12 a wani rikici da ya wakana a jahar a ranar Lahadi.
Kakakin ‘Yan sandan jahar ne ya bayyana hakan a lokacin da yake ganawa da manema labari.
Tyopev Terna, yace tsintuwar gawar wani matashi mai suna Enoch Monday, itace ta jawo wannan lamari.
Sai dai ya kara da cewa wannan tashin hankali ya faru ne a garuruwan Unguwan Damisa da kuma dutse Uku da ke karamar Hukumar Jos, ta Arewa, a jihar ta Filato.