Rahotanni daga Jihar Ondo na nuni da cewa an rufe jami’ar kimiya da fasaha ta Olusegun Agagu dake jihar bayan samun rahotanni yiwa wasu yan mata huɗu fyade.
A ranar Alhamis ne ɗaliban jami’ar suka fito mararan suka nuna tashin hankalin su bisa yawaitar fashi da makami gamida yawan fyade da ake ganin makobtan makarantar ne ke kutsawa.
Yayin zanga-zangar, daliban sun killace duk wata hanya da ta hada da jami’ar, lamarin da ya sa masu ababen hawa komawa da baya.
Da yake tabbatar da aukuwar waɗannan al’amura, shugaban Daliban makarantar Damilola Okunomo ya ce yanzu kam tura ta kai bango game da tabarbarewar tsaro a jami’ar don haka dole ne su nuna ɓacin ransu.
Ya ce wasu bata gari na shiga dakunan Kwanan Dalibai su karbe musu wayoyi da na’urorin kwamfuta da dai sauran kayayyaki masu muhimmanci gamida yiwa dalibai mata fyade, amma hukumar makarantar ta nade hannunta ta zauna.