Dr Tunde Arosanyin mashawarci na musamman ga kungiyar manoman Nijeriya ta AFAN ta roki gwamnatin tarayya da na jihohi da su cire manoma a cikin wadanda dokar zaman gida ya shafa a wani mataki na dakile yaduwar Korona.
Arosanyin, ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a Abuja, inda hakan zai bai wa manoma damar yin noman da za su wadata ‘yan kasa da abinci domin dakile yaduwar yunwa.
Arosanyin ya nemi kafin karshen watan Afrilu a cire manoman a cikin dokar domin wadata kasarnan da abinci.