An rantsar da babban lauyan Najeriya, SAN, Mista Y.C Maikyau ranar Juma’ar nan a matsayin sabon shugaban kungiyar lauyoyin Najeriya, NBA bayan karewar wa’adin mulkin Olumide Akpata.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Maikyau, wanda aka rantsar a matsayin shugaban NBA na 31, ya lashe zaben da aka gudanar a farkon watan Yuli da kuri’u 38,000.
A wajen bikin rantsuwar wanda ya gudana a Eko Hotel & Suites, Maikyau ya godewa Allah da ya bashi damar.
Karanta kuma: ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Sun Hallara A Taron NBA
Ya kuma mika godiyarsa ga takwarorinsa na YC Maikyau & Co., da tawagar yakin neman zabensa, da abokansa da abokan huldar da suka mara masa baya.
Sabon shugaban ya yabawa gwamnatin Akpata da ba ta bar baya da kura ba bisa gagarumin nasarorin da ta samu a kungiyar NBA cikin shekaru biyu da suka gabata.
Ya yi alkawarin ba wai kawai ya ci gaba da ci gaba da samun nasarori da ayyukan da gwamnatin Akpata ta samu ba har ma da ci gaba a kai hakan.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa, Ya mika hannun sada zumunci ga duk wadanda suka tsaya takara a ofishin Shugaban NBA tare da shi, yana mai cewa shi da tawagarsa za su rika zuwa su yi amfani da zurfin iliminsu daga lokaci zuwa lokaci.
“Na ga duk manyan bayanan ku da shawarwarinku masu kyau na NBA. Abin da ya faru shi ne, yanzu mu ne aka dora wa alhakin. Ina gayyatar ku da ku ba mu hadin kai yayin da muke gina kungiyar lauyoyi ta Najeriya zuwa wannan babban matsayi da dukkanmu muke so,” inji shi.
A wani labarin kuma: Wani Lauya ya Maka Ƙungiyar su Ta Lauyoyi a gaban Kotu
Okafor-Oyilo a rubutun da yayi, wanda ƴan Jarida suka samu a ranar Talata, yace ya rubuta ra’ayin sa ne ga Mataimakin Gwamnan Jahar Anambra na Lokacin, wanda kuma shine Shugaban Kwamitin Sasanci akan Ƙasa a Al’ummomin Ukpo da Abba a Jahar Anambra.
A cewar sa, wannan ra’ayin wasu suka fitar dashi akan wannan rikicin Kasa.