Wakilinmu Mohammed Gambo Yobe
Bukin rantsar war ya gudana ne a sabon dakin taro dake gidan gwamnatin jahar Yobe, a birnin Damaturu.
A jawabin sa jim kadan bayan ya karbi karagar mulkin, Gwamna Mai Mala Buni yayi alkawura da dama ga ‘yan jahar Yobe.
Na farko, yayi alkawarin biyan sabon albashi ga ma’aikata Naira dubu 30, sa’annan ya saka dokar ta baci bangaren ilimi.
Daga bisani ya nemi goyon baya daga al’ummar jahar domin sauke nauyi dake kansa.