Daga: Ibrahim Hassan Hausawa
Hukumomin Jami’ar Arthur Jarvis da ke Jihar Kuros Riba sun rufe makarantar har zuwa wani lokaci bayan sace wata daliba da aka yi a daren ranar Talata.
Mukaddashin magatakardar jami’ar mai zaman kanta, Ughas Ngozi Felicia, ta bayar da sanarwar a ranar Laraba inda ta umurci iyaye da masu kula da su da kwashe ‘ya’yansu daga harabar jami’ar cikin sa’o’i 24.
KARANTA WANNAN LABARIN: https://dimokuradiyya.com.ng/rikicin-takara-gwamnan-adamawa-a-apc-kotu-ta-tsayar-da-hukunci-kan-nuhu-ribadu-da-yake-yiwa-binani/
Sanarwar ta ce, daliban da ke rubuta jarabawar a halin yanzu za su ci gaba da karatu a zangon karatu na gaba, yayin da daliban shekarar karshe za a sanar da su sabon cigaban da aka samu a nan gaba.
Sanarwar ta ce, “Hukumar ta amince da fara hutun zangon karatu na 2021/2022 daga ranar Laraba, 20 ga watan Yuli, 2022.
“Dukkan daliban ana sa ran su fice daga harabar jami’ar. Za a sanar da ranar da za a ci gaba da zangon karatu a lokacin da ya dace.
“Duk jarabawar da ta yi fice za a yi ta ne a farkon zangon karatu na gaba. Za a sanar da ɗaliban shekarar ƙarshe game da kwanan wata/ cikakkun bayanai na Tsaron Aikin su.”
Majiyar JARIDAR DIMOKURADIYYA ta tattaro cewa Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba sun yi garkuwa da wata daliba tare da jikkata wasu dalibai a lokacin da suke kokarin tserewa a daren ranar Talata a yayin da daliban ke dawowa daga karatun dare.