Kasar Chana ta sake samun mutum 21 dauke da cutar Korona a ranar Asabar, a daidai lokacin da cutar ta sake bulla a birnin Beijing.
Dukkan mutum goma sha bakwai da aka same su da cutar, su dauki cutar ne a birnin kasar, kamar yadda sabbin rahotannin masu dauke da cutar ya nuna.
Bayanai sun nuna cewa mutum hudu kuma shigowa suka yi da cutar, inda aka same su a garuruwan Guangdong, Gansu, da Shanghai.
Sabbin wadanda aka samu da cutar, ya sabawa hasashen da hukumar lafiyar ta yi.