Yan bindiga da suka yi garkuwa da babban malamin jami’ar Jos mai suna Dakta Dan Ella sun sake shi.
A ranar Alhamis ne dai yan bindigar suka saki Ella inda kuma tuni aka dauke shi zuwa gidansa dake kan hanyar Jos zuwa Bauchi a birnin na Jos.
A ranar laraba ne yan bindigar suka yi garkuwa da malamin a rukunin gidaje na Haske Quarters dake Unguwar Lamingo cikin birnin na Jos ta karamar hukumar Jos ta Arewa.
Sa dai duk da sakinsa a ranar Alhamis din, a yau ne shugaban kungiyar malaman jami’o’i ta jami’ar Dakta Lazarus Maigoro ya tabbatar da labarin.
Daga bisani ya bukaci hukumar gudanarwar jami’ar da ta tashi tsaye don ganin an kiyaye aukuwar hakan a nan gaba.