Daga: Abbas Yakubu Yaura
An samu gawarwakin wasu dalibai biyu na Jami’ar Jihar Kwara (KWASU), Malete, Tobiloba Daniel da kuma masoyinta, Arewa Abayomi, a dakin kwanan dalibai na Daniel.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya ruwaito cewa wadanda suka mutun dukkansu dalibai ne masu matakin aji na 200 kuma suna tsaka rubuta jarabawa ne kafin faruwar lamarin.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yajin Aikin ASUU: FG Ta Gayyaci NUC,VCs Zuwa Taro Na Musamman
Da take mayar da martani kan lamarin, Daraktar hulda da jami’a ta KWASU, Dakta Saeedat Aliyu, ta ce babu wata sanarwa a hukumance kan lamarin.
Sai dai kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Ajayi Okasanmi, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce: “Bayanan an gano gawar dalibai biyun a cikin dakinsu, kuma an sanar da ‘yan sanda.
“Jami’an mu ne suka rugo kofar sannan aka kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilorin (UITH) domin a tantance su.”
“Ana ci gaba da bincike kan lamarin,” in ji Okasanmi.
A wani labarin kuma Da Dumi-dumi: Tinubu, Shettima, Gwamnonin APC Sun Dira Gidan Jonathan
Asiwaju Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, ya jagoranci manyan jiga-jigan jam’iyyarsa zuwa gidan tsohon shugaban kasa Goodluck.
Cikin wadanda suka ziyarci tsohon shugaban kasar akwai Sanata Kashim Shettima, dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar APC, da gwamnoni biyar.