Gwamnatin Tarayya ta fitar da jadawalin jarrabawar ɗaliban da ke ajin ƙarshe a makarantun Sakandire.
Ƙaramin ministan ilimi, Honorabul Chukwuemeka Nwajuiba ne ya bayyana hakan, inda ya ce za a gudanar da jarabawar ne daga ranar 17 ga watan Agusta zuwa 18 ga watan Nuwamba.
A yayin da ita kuma Jarabawar NABTEB za a fara ne daga 21 ga watan Satumba zuwa 15 ga watan Oktoba.
Sannan za a fara jarabawar NECO ce daga ranar 5 ga watan Oktoba zuwa 18 ga watan Nuwambar 2020.