Jam’iyyar APC reshen Birtaniya sun nemi zababben gwamnan jihar Bayelsa a karkashin jam’iyyar APC din, David Lyon da ya dubi nasarar da ya samu wajen lashe zaben gwamnan jihar a matsayin wani nauyi na yiwa al’umma aiki.
Ade Omole, shugaban jam’iyyar reshen, shi ne ya bayyana hakan a yayin zantawarsa da manema labarai a ranar Litinin a Abuja a lokacin da yake bayyana ra’ayinsa kan nasarar da jam’iyyar ta samu a Bayelsa.
Ya bayyana nasarar da APC ta samu a matsayin yadda masu zabe suka amshi jam’iyyar ba tare da nuna bangarenci ba.
A cewarsa, nasarar da David Lyon ya samu bayan PDP ta kwashe shekara 20 tana mulkin jihar, ya karyata batun cewa ba a san jam’iyyar APC a wadansu sassan kasarnan ba.
Rahotanni sun bayyana cewa INEC ta bayyana cewa dan takarar APC wato Davi Lyon ya samu kuri’a 352,552 yayin da dan takarar PDP wato Duoye Diri ya samu kuri’a 143,172.