By Abbas Yakubu Yaura
Wasu da ake zargin ’yan kungiyar asiri ne sun farmaki wani direban babur din (okada) na kasuwanci a Kuto, dake Abeokutan jihar Ogun.
Wakilinmu ya tattaro cewa an sari wanda abin ya shafa ne da adduna a kai da misalin karfe 2:30 na rana a cikin Kuto dake karkashin gada.inda maharan suka bar wanda iftila’in ya rutsa dashi a cikin jini.
Wani ganau ya shaida wa wakilin jaridar Dimokuradiyya cewa ‘yan bindigar da suka sanya abin rufe fuska sun zone cikin ayarin babura uku.
Majiyar ta ci gaba da cewa, ‘yan bindigar sun bi sahun wanda aka farmaka ne daga Bolevard na fadar shugaban kasa dake kan titin Oke Mosan zuwa yankin Kasuwar Kuto.
“Sun tare mahaya a mahadar hanyar Kuto, suka far masa da sara da adduna a kai, lamarin da ya kai ga barkewar annoba.”
An ce wadanda ake zargin ’yan kungiyar asiri ne sun yi tsalle sun haye kan baburan su inda suka tsere daga yankin.
Daya daga cikin direban babur wanda ya yi ikirarin ya shaida lamarin, yace da farko an harbe wanda aka farmaka kafin a kai masa hari da adduna.
Lokacin da wakilinmu ya ziyarci wurin, yaga wanda abin ya shafa cikin jini akwace, Har ya zuwa lokacin da wakilinmu ya bar yankin, ba a kai ga samun taimako ga wanda abin ya shafa ba.
Munyi Kokarin yin magana da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Abimbola Oyeyemi, hakan mu ya ci tura saboda ba a iya samunsa ta wayar tarho.Sakon kartakwana da aka aika masa bai amsa ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.