‘Yan adawa a Sudan sun kira wani yajin aikin gama gari kama daga yau Lahadi don tilastawa majalisar Sojin kasar mika mulki zuwa farraren hula. Matakin dake zuwa kwanaki biyar bayan sojojin kasar suka bude huta saman masu zanga-zanga a Khartoum. Wasu rahotanni na nuni cewa Jami’an tsaro sun kame wasu tsoffin ’yan tawayen kasar, da kuma jagoran ‘yan adawa. Duk da kokarin mai shiga tsakani, Firaministan Habasha Abiy Ahmed a Khartoum, wanda a Juma’a ya isa birnin domin sasanta shugabannin masu zanga-zangar da bangaren sojoji don sake maido da tattaunawar da suka yi watsi da ita, kungiyoyi na ci gaba da bayyana damuwa ganin halin da kasar ke ciki yanzu haka.