Ministan yaɗa labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed ya ce Hukumar Kula da Gidan Rediyo da Talabijin ta Najeriya (NBC) ta ƙara yawan tarar da za a ci duk gidan rediyo ko talabijin da ya ba da kafar yin kalaman batanci zuwa Naira miliyan biyar.
Ministan ya bayyana hakan ne a wajen bikin ƙaddamar da sabon kundin dokokin yaɗa labarai bugu na shida a ranar Talata.
Hukumar ta hukunta gidajen kafofin yada labarai 31 wadanda suka yi ƙarya a game da COVID-19 da kalaman ƙiyayya da sauransu.
Lai Mohammed ya ce an yi ƙarin tarar ne daga N500,000 zuwa miliyan biyar saboda rashin bin doka da kafofin yaɗa labaran suka yi yayin manyan zaɓukan shekarar 2019.
https://dimokuradiyya.com.ng/gwamnatin-buhari-ta-%c6%99wato-naira-biliyan-800-lai-mohammed/
“A lokacin zaɓen na 2019, idan ’yan siyasa suka tunkari kafofin yaɗa labarai da batancin da suke son yi a kan wasu aka ki sanyawa, sai su biya kuɗin da za a biya tarar ta N500,000 har da riba.
“Duk da miliyan biyar ɗin da muka ƙara, idan kafar watsa labarai ta biya amma ba ta daina bayar da damar yin kalaman ɓatanci ba, to ba mu da wani zaɓi sai mu kwace lasisin ta”, cewar Ministan.
Ya ce canje-canjen da aka samu a sabon kundin dokokin yaɗa labaran dai sun fi yawa ta fannin harkokin siyasa da labaran gida da tallace-tallace da kuma hana gasa.
A baya dai an zargi gwamnati da yunƙurin amfani da dokokin hana kalaman batanci don haramta wa masu suka da ’yan adawa damar faɗin albarkacin bakinsu.