Wata babbar kotu dake zamanta a jihar Kano ta yi watsi da karar da tsohon sarkin Kano Muhammadu Sunusi na II ya shigar kan kotun da ta dakatar da hukumar karbar koke-koke da yaki da cin-hanci ta jihar, bisa yunkurinta na tuhumarsa kan karkatar da dukiyar masarautar.
Mai Shari’a Lewis Allagoa ya hukumar karbar koke-koke da yaki da cin-hanci karkashin jagorancin Barista Muhyi Magaji Rimin Gado bata karya wata doka wadda ta shafi kare hakkin dan Adam ba kamar yadda tsohon sarkin ke ikirari.
Shugaban hukumar tare da wasu lauyoyi daga dake kare bangaren gwamnati sun wakilci gwamnan jihar Dakta Abdullahi Umar Ganduje a yayin zaman kotun.
https://dimokuradiyya.com.ng/yadda-gwamna-ganduje-ya-nada-sabon-sarkin-rano/
Kafin sauke shi daga kan karagar mulki a 9 ga watan Maris, Sunusi na II ya kai da kara kotu a ranar 5 ga watan Maris domin kotun ta dakatar da hukumar ga gayyatar da suke masa bisa zargin karkatar da dukiyar masarautar Kano.
Idan ba a manta ba a watan Nuwambar shekara ta 2019, mai Shari’a Obiorah Egwuatu yasa a yi bincike kan zargin karkatar da kudin masarautar kimanin biliyan 3.4.
Sai dai kafin sake wani zaman kotun gwamnatin jihar Kano ta tube shi tare da nada dan gidan marigayi Ado Bayero, wato Aminu Ado Bayero a matsayin sabon sarkin Kano.