Wani matshi a Jihari Niger mai suna Abubakar ya turmushe wani yaro mai suna Aminu dan shekara 12 inda ya dunga luwadi dashi har sai da ya rattaka masa dubura Wanda hakan yai sanadiyar rasa ransa.
Wannan dai mummunan aikin ya faru ne garin kwantagora ta Jihari Niger
Shidai wannan shu’umi ya sace wannan yaro ne dan shekara 12. Makotan Abubakar sunji kara da ihu na yaro sai suka garzaya gurin yan sanda.
Tuni yan sanda suka damke shi shi kuma yaron aka garzaya dashi asibiti Wanda anan yace ga garinku nan.
Majiyar mu tace daga nan yan sanda suka gurfanar dashi gaban kotu kafin yaron ya mutu.
Amma abun takaci sai alkalin kotun magsitare din ya yankewa Abubakar zaman gidan kaso na wata daya da kuma biyan kudin tara N300,000
Madogara: NTA