An yi garkuwa da Cif Dennis Ekpe Ogbu, daya daga cikin kwamishinonin Gwamna Samuel Ortom na jihar Benue.
Majiyar Dimokuradiyya ta tattaro cewa wanda abun ya shafa yana rike da mukamin kwamishinan gidaje da raya birane an yi garkuwa da shi ne a hanyar Ado-Otukpo a jihar.
KU KARANTA KUMA Wasu Mutane Uku Sun Rasa Ransu A Wani Kauyen Jihar Binwai
Rahotanni sun bayyana cewa Ogbu yana tafiya ne zuwa karamar hukumarsa ta Ado, inda masu garkuwan suka tilasta wa motarsa kirar Hilux tsayawa a mahadar Adankari da misalin karfe 9 na dare sannan suka tafi da shi.
Jaridar Daily trust ta tattaro cewa yayin da ‘yan sanda suka kwato motar kirar Hilux, har yanzu ba a san inda kwamishinan yake ba.
Jami’ar hulda da jama’a ta ‘yan sanda (PPRO), SP Catherine Anene, ta tabbatar wa wakilan afkuwar lamarin ta wayar tarho.
“Tabbas lamarin ya faru, muna kan hanyarmu ta zuwa yankin, zan ba ku ƙarin bayani idan muka isa wurin,” in ji Anene.
Sace-sace da kashe-kashe dai na karuwa a sassa daban-daban na kasar duk da tabbacin da gwamnati ta yi na cewa jami’an tsaro na kan gaba a lamarin.
A jihar Katsina kadai an yi garkuwa da mutane 46 a karshen makon da ya gabata. An yi rawaito irin wadannan hare-hare a jihohi daban-daban.
Magance matsalar rashin tsaro ya kasance a sahun gaba na yakin neman zaben 2023.
A Wani Labari Kuma PDP Ta Nada Dogara A Matsayin Dan Kwamitin Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa
Kwamitin yakin neman zaben (PCC) a ranar Lahadi ta sanar da tsohon kakakin majalisar wakilai, Yakubu Dogara, a matsayin mamba na kwamitin “nan ta ke”.
Babban Darakta na kwamitin jam’iyyar PDP a yakin neman zabe PCC, Aminu Tambuwal, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ya ce nadin Dogara “yana daga cikin ayyukan da muke ci gaba da yi na hada kai da dan takararmu na shugaban kasa, Atiku Abubakar, domin mu maido da martabar babbar kasar mu Najeriya”.