An bude filin jirgin ne a kokarin ci gaba da ayyukan sufurin jiragen sama a fadin kasar nan, bayan rufe tashoshin jirgin sama tsawon watanni uku da suka gabata sakamakon bullar cutar Sarƙe numfashi.
Rahotanni sun ce an dauki matakan dakile yaduwar cutar a filin jiragen na Abuja da na Legas ta hanyar sanya alamun ba da tazara a wuraren da jama’a ke bin layi da ilahirin kujerun zama a harabar tashoshin da kuma kujerun cikin jiragen sama.
Kamfanin dillacin labarai na ƙasa (NAN) ya rawaito cewa, an tanadi kayayyakin kariyar cutar Korona a tashoshin jiragen saman da suka hada da na’urori da sinadaren wanke hannu.
https://dimokuradiyya.com.ng/an-kara-waadin-bude-tashoshin-jiragen-sama-na-nijeriya/
An kuma zana alamomin ba da tazara, baya ga na’urorin gwada yanayin jiki da manyan injina guda biyu da za su rika aikin tantance fasinjoji da aka tanadar.
Rahoton ya ce an kwashi ‘yan jaridan da ke ba da rahoton ayyukan Hukumar dakile yaduwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) daga tashar jirgin sama ta Murtala Muhammad da ke jihar Legas zuwa tashar jirgin saman birnin tarayya, Abuja a matsayin gwaji, inda suka shaida matakan kariyar da aka tsara a tashoshin.
A ‘yan makwanin da suka shude, Hukumar Sufurin Jiragen Sama ta Najeiriya ( NCCA) ta sanar da shirin bude tashoshin jirgin sama domin ci gaba da harkokinsu bayan an rufe su a wani mataki na yaƙi da cutar Korona.