A yau Lahadin aka binne gawar tsohon ministan noma da albarkatun ruwa a zamanin gwamnatin marigayi shugaba ‘Yar’aduwa, Dakta Abba Sayyadi Ruma a Katsina.
An binne gawarsa ne a makabartar Danmarina, inda aka yi jana’izar marigayi Shugaba ‘Yar’aduwa da wasu fitattun mutane bayan sallar jana’izar da aka yi a masallacin Juma’a na GRA da misalin karfe 12 na ranar Lahadi.
Sallar jana’izar wadda ta samu halartar dimbin jama’a, ta samu jagorancin fitaccen malamin nan na Kano kuma tsohon kwamandan Hizba, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa.
Daga cikin manyan baki da suka halarci sallar jana’izar sun hada da hamshakin dan kasuwa dan asalin jihar Katsina, Alhaji Dahiru Bara’u Manga,l da babban darakta na SMEDAN, Dr Dikko Umar Radda da sauran ‘yan uwa da abokan arziki na marigayin.
KARANTA WANNAN LABARIN: Iran ta Zargi Amerika Wajen Cimata Dunduniya
A cikin sakon ta’aziyyar Dr Radda ya bayyana marigayi Ruma a matsayin hazikin dan Katsina, wanda ya yi fafutukar ganin an samu ci gaban siyasa da ilimi da tattalin arzikin al’umma gwargwadon iyawarsa.
“Muna rokon Allah ya gafarta masa kurakuransa, kuma ya ba shi Jannatul Firdaus.
“Muna kuma gode wa duk wadanda suka zo daga nesa da kusa domin nuna alhini tare da jajanta mana kan wannan rashin kuma muna rokon Allah ya mayar musu da su lafiya,” inji shi.
Shima a nasa sakon, sakataren gwamnatin jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa, ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga Katsina, har ma ga kasa baki daya.
Ya kuma yi addu’ar Allah ya jikansa da Jannatul Firdaus da iyalansa da kuma jiharsa baki daya, ya jikan wannan rashi.
Comments 1