- Ana zargin Jami’an ƙasar Myanmar da bankawa wani ƙauye wuta.
- Jaridar Aljazeera Aljazeera ta ruwaito cewar ranar talatar da ta gabata ne wani ƙauye me suna Kin Ma, mai kimanin mutane 800 da gidaje 200 aka wayi gari ya koma toka.
- Jami’an tsaron sun bankawa kauyen wuta ne bayan gamzawa da mutanen ƙauyen sukayi da abokan aikin su, inda labari ke zuwa lamarin ya janyo mutuwar wasu tsofaffi biyu.
Lamarin dai ya janyo zanga-zanga a sassan ƙauyukan da sauran garuruwan dake ƙasar jin kadan bayan labarin aika-aikar da jami’an tsaron sukayi a ƙauyen.
KARANTA:-
Gwamnan jihar neja ya kaddamar da Kungiyar ‘Yan sakai don wanzar da tsaro
Gidan talabijin na MRTV dake ƙasar ya ruwaito cewar “aukuwar lamarin a ranar talata a yayin da wani ƙauye me kimanin mutane 800 da gidaje 200 an wayi gari ya koma toka, wasu yan ta’adda ne ake zargi da Wannan aika-aikar”
Gidan talabijin din yace “labarai dake ta yawo kancewar jami’an tsaron ne suka bankawa ƙauyen ba gaskiya bane kuma wannan yana nuna rashin girmama Jami’an ƙasar.
Haka kuma gidan jaridar Reuters sunyi kokarin bin diddiƙin lamarin inda suka kira mai magana da yawun jami’an tsaron amma bai samu ɗaya wayar ba.
Wani ɗan ƙauyen yace jami’an tsaron ne suka bankawa garin wuta saboda ƙalubalantar da mutanen ƙauyen sukayi.
Wani matashin mai kimanin shekaru 32 da wanda ke basu agajin gaggawa ya ce mutane biyu suka rasa ransu saboda suma sun tsufa da yawa basu iya gudu.
A WANI LABARIN:-
Kamfanin MTN sun ce da akwai samun karancin sabis saboda tashin hankalin dake faruwa a kasar nan.
Kamfanin ya bayyana cewar da yiwuwar samun karancin sabis duba da irin rikice-rikicen dake tashi a ko wane yanki dake fadin kasar nan.
Wannan shi zai kawo cikas lokacinda zamu aika masu gyara don cigaban sabis din.
Nigeria tana yin bakin kokarinta wajan fada kungiyar Boko Haram tun bayan sama da shekaru masu yawa, gami da satar mutane don biyan kudin fansa, yin awon gaba da dalibai da kuma tafiya da shanun a yankin kudu maso gabas na kasar najeriya.
A gabas maso arewan dake ƙasar, sannan da jihohin Najeriya ta tsakiya farmakin yan ta’addan ya janyo asarar rayukan mutane wanda ba a san adadinsu ba da miliyoyin kudade