Gwamnatin tarayya ta hannun ma’aiktar jin kai da kula da walwalar jama’a ta kasa, ta cigaba da rabon tallafin kudi naira 15,768 ga magidanta da masu kananan karfi a jihar Anambra. Karkashin shirin ta na bayar da tallafin kudi a hannu.
Shugaban sashin kula da rabon kudin a jihar Anambra Mr Ralph Enukorah, a yayin ganawarsa da manema labarai ya ce wadanda suka amfana da shirin an zabo su ne daga kananan hukumomi 11 cikin 21 da jihar ke da su baki daya.
Ya kuma ce sun fara rabon ne da wasu kananan hukumomi shida wadanda suka fi yawan masu karamun karfi wadanda suka hadar da Awka ta arewa Dunukofia, Ihiala, Anambra ta yamma Anyamelum Orumba ta kudu.
Mr Enukorah ya tabbatar da cewa daukacin wadanda suka mafna da tallafin sun godewa gwamnatin tarayya bisa wannan ayyukan alkhairi da take cigaba da yiwa yan kasa.