By Abbas Yakubu Yaura
Tsohuwar Ministar Ilimi, Oby Ezekwesili, ta yi kira ga Majalisar Dokoki ta kasa da ta gayyaci Shugaban kasa Muhammadu Buhari domin ya yi bayani kan matsalar rashin tsaro a kasar.
Ezekwesili ta yi wannan kiran ne a matsayin martani ga fille kan wani dan majalisar dokokin jihar Anambra, Okechukwu Okoye da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba suka yi.
An gano kan Okoye, ba tare da gangar jikin sa ba a ranar Asabar a Nnobi, cikin karamar hukumar Nnewi ta Kudu a jihar Anambra.
Wannan ci gaban ya faru ne kwanaki bayan sace shi.
An yi garkuwa da dan majalisar Anambra, mai wakiltar mazabar Soludo a makon jiya.
Da take mayar da martani, Ezekwesili ta wallafa a shafinta na Tuwita cewa: “Wataƙila yanzu da @nassnigeria ta ga cewa ƴan uwansu ‘yan majalisa a jihar Anambra za su iya yi musu muguwar dabi’a da muggan laifuka, daga ƙarshe kuma za su sami bakin jini wajen GAYYATAR babban kwamandan sojojin Nijeriya @MBuhari zuwa wajen don Ƙarfafa kawar da Rashin Tsaro a Ƙasar.
“Na daina damu na nemi @MBuhari ya yi komai sau 3 a jere har zuwa shekarar da ta gabata, ganin yadda ya rabu da kasa mai gazawa, sai kawai mutum ya nemi auna tunaninsa da na jiki na karfinsa na ci gaba da aiki a matsayin @NGRPresident.” Shi ke nan.”