Wakilinmu Sale Hussain Takai Jigawa
Sakataren zartarwa na Hukumar bada Agajin gaggawa a jahar Jigawa Mal. Yusuf Sani
Babura, yayi kiran ne a lokacin da yake ganawa da wakilinmu a Ofishinsa.
Mal. Yusuf Babura, yaci gaba da cewa, a bara Ambaliyar Ruwan ta shafi Kananan Hukumomi goma sha tara(19), Dubunnan Mutane sun rasa Gonakin su, wasu dubunan Gidaje, wasu Kayan Abinchi, wasu kuma duka suka rasa, haka kuma an rasa Rayukan wasu mutanen.
Dan haka sai Malam Yusuf Sani ya hori mutanen jahar ta Jigawa da cewa, su daina
zuba shara ko Taki a magudan Ruwa, hakan yakan haddasa ambaliya a garuruwanmu.
Sakataren yaja hankalin malaman Tsaftar a Jahar dasu rika kula da irin wadannan
matsalolin da ka’iya jefa jahar cikin mummunar matsala.
Sakataren yace, a bara, sun karbi yan’ gudun shijira kusan dubu Ashirin da Takwas (28,000) inda Hukuimar bada Agaji ta dauki nauyin Abincin su, da Suturun su, da gurin kwana, sai da Ruwa ya janye, suka koma Gidajensu, hakace tasa bana mukayi managarcin hiri, tun kafin abin ya faru, bayan haka mun tanadi fatun buhunhuna dan yin jingar tarewa Ruwa, kamar yadda muka sabayi duk shekara.
A karshe Yusuf Sani Babura yace, yanzu haka Hukumar bada Agajin gaggawa ta Gwamnatin Tarayya ta kawo tallafin Iri maiyi da wuri, wanda za’a bawa mutane dubu saba’in (70,000), dan haka sai ya nemi, hadin kan Al’umar jahar ta Jigawa, dasu baiwa ma’aikatan hukumar bada Agajin ta kasa, data jaha dukkan hadinkan da ya kamata.
A lokacin da suka ziyarci garuruwansu, dan gudanar da wani aiki, kuma a basu amsar
data dace da tambayar da sukayi dan gudun korafi, bayan kamala tantancewar da ake kan yi a yanzu, domin idan ba’a tantanceka ba, ba wani tallafi da zaka samu.