Shugaban jam’iyyar APC na jihar Sokoto ya zargi gwamnatin jihar
Jam’iyyar APC reshen jihar Sokoto, ta bukaci gwamnatin jihar da ta dakatar da shirin mikawa kananan ma’aikata albashi daga ma’aikatar kananan hukumomi zuwa kananan hukumomi.
Karanta kuma: PDP Ta Caccaki Jam’iyyar APC Kan Kiran Da Ta Yi Na A Tsige Gwamnan Arewa
Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alhaji Isa Sadiq-Achida ne ya bayar da wannan shawarar a wata sanarwa da ya aikewa kamfanin dillancin labarai na Kasa NAN a Sokoto ranar Asabar din nan.
Sadiq-Achida ya ce, “shiyyar jihar ya samu cikakken labarin matakin, wanda aka yi niyyar amfani da shi a matsayin makamin siyasa kan ma’aikatan da ake zargi da goyon bayan jam’iyyun da ba jam’iyya mai mulki a jihar ba.
“Yana da kyau a lura cewa, shekaru da yawa yanzu, ana ta kiraye-kirayen a ba da ‘yancin cin gashin kai ga kananan hukumomi, kamar yadda yake kunshe a cikin dokokin da suka dace.
“Gwamnonin da suka gabata a Jihar sun yi hakan. Amma, abin takaici, kiraye-kirayen sun fado kunnuwa.
“Duk da haka, a cikin ‘yan makonnin da suka gabata, sakamakon rashin jin dadi da jam’iyyar PDP ta samu a gwamnatin Sokoto, ma’aikatar kananan hukumomi ta sanar da shirin mika albashin ma’aikata.
“Don haka bari in yi gargadin cewa jam’iyyar APC za ta bijirewa duk wani yunkuri na tauye hakkin kowane dan kasa mai bin doka ta hanyar hana shi albashi, saboda dalilai na siyasa.
“In ba haka ba, ta yaya gwamnatin da ta bijirewa duk kiraye-kirayen ‘yan kasa masu ma’ana, cikin shekaru uku da suka gabata, kwatsam za ta yanke shawarar gabatar da wannan matakin.
Shugaban jam’iyyar APC ya kara da cewa sabuwar soyayyar da gwamnatin jihar ta samu na ma’aikatan kananan hukumomi abin mamaki ne da kuma shakku.
“Idan da gaske gwamnati da gaske take kuma da gaske take son inganta tsarin kananan hukumomi a jihar, ya kamata ta cika alkawarin da ta dauka na biyan Naira 30,000 mafi karancin albashi ga ma’aikatan kananan hukumomi da malaman makarantun Firamare.
“Ya kamata ta sake sakin kudaden kananan hukumomi da ake tsare da su kuma muna da dalilin da za mu yi imani cewa galibi ana karkatar da su ba bisa ka’ida ba zuwa wasu dalilai marasa tushe,” in ji shi.
Ya ce sahihancin gwamnati zai baiwa kananan hukumomi damar aiwatar da ayyukan canza rayuwa ga al’ummarsu.
Sadiq-Achida ya ce, “wannan ita ce hanya mafi inganci da dacewa wajen sauya tsarin kananan humumomi da inganta harkar tsaro a jihar tare da samar da rayuwa mai inganci a yankunan karkara.”
Karanta Anan: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Kararrakin Da Aka Shigar Da Shugabannin APC A Sokoto
Da yake mayar da martani kan zargin, Alhaji Abdullahi Hausawa, kakakin jam’iyyar PDP a jihar ya ce an yi hakan ne domin kara baiwa kananan hukumomi iko.
“Wannan tsari ne da aka saba yi tun da dadewa, amma daga baya bayan shawarwarin kwamitin tantancewa, an mayar da albashin kananan jami’an zuwa ma’aikatar.
“Don haka matakin da gwamnatin jihar ta dauka ya biyo bayan kiraye-kirayen da jama’a suka yi na a baiwa kananan hukumomin karfi, don kara musu kwarin gwiwa da kuma tabbatar da ma’aikatan sun himmatu wajen gudanar da ayyukansu.
“Bugu da kari, akwai manya da kananan jami’ai da dama da ke goyon bayan jam’iyyun siyasa daban-daban kuma gwamnati ba ta dakatar da albashin su ba kamar yadda APC ta yi zargin,” inji shi.
Hausawa, wanda kuma shi ne kwamishinan harkokin cikin gida, ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na ci gaba da kare hakkin duk wani dan kasa a jihar, ba tare da la’akari da siyasa ko addini ba.
(NAN)