- Tsohon gwamnan Ribas, Nyesom Wike, ya bayyana cewa gwamnatin jam’iyyar APC ta sake samun damar gyara kura-kuranta.
- Tsohon gwamnan ya caccaki PDP da rashin bin ka’idojin shiyya-shiyya wanda ya ce ya janyo musu hasara a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu.
- Jagoran gwamnonin G5 ya bukaci masu suka da su nuna goyon bayansu ga gwamnati mai ci.
Tsohon gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, ya bayyana cewa an sake baiwa gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki damar gyara abin da ya bayyana a matsayin zaluncin da suka yi wa ‘yan Najeriya a baya da jam’iyyar adawa ta PDP,kamar yadda Punch ta rawaito.
Wike ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da manema labarai kai tsaye, Talata a babban birnin jihar, Fatakwal.
KARANTA WANNAN: Martanin APC Kan Rusau Din Abba Gida-Gida
“Ya kamata APC su rika murna da cewa Allah Ya ba su dama a kan PDP. Allah ya baiwa APC damar tuba daga laifukan da suka yi wa ’yan Najeriya,” inji Wike.
Tsohon gwamnan ya sake caccakar jam’iyyar PDP da rashin bin ka’idojin shiyya-shiyya wanda ya ce ya janyo musu hasarar zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu, ya kuma baiwa APC damar samun nasara.
Ya kuma bukaci masu suka da su nuna goyon bayansu ga gwamnati mai ci ta yadda za a samar da ribar dimokuradiyya ga ‘yan Najeriya.
“Allah ya ba su wannan dama a yanzu kuma suna son sake cushe ta ta hanyar kawo rikici,” inji shi.
“Idan Shugaban kasa ba shi da tsarin tafiyar da al’amuran yau da kullum, wa ke shan wahala? Shin ba ’yan Najeriya ba ne? Mu yarda cewa dukkanmu daya ne, mu baiwa kowa fahimtar nasa.”
Da aka tambaye shi ko zai amince da nadin da shugaba Bola Tinubu zai yi masa, Wike ya bayyana cewa ba ya bara amma zai yi sha’awar ko wane matsayi zai yi aiki idan aka ba shi.
“Da farko dai, ba yi ra’ayin neman mukami ba, saboda Kristi. Kuma ba zan iya zama mai mahimmanci ba saboda kun ba ni mukami. Ina nufin, ya kamata ku duba sosai.
“Na biyu, Shugaban kasa bai kira ni ba. Tare da girmamawa, idan Shugaban ya kira ku ya ce, Ina so ku yi hidima. Watakila zan tambaya, a wane matsayi kuke so in yi hidima? Kuma ya ce shi, na ce lafiya, na gode, yallabai.
“Duba ina da ƙungiyar siyasa, ina da iyali, ba zan zauna ba tare da magana da kowa ba na ce eh. Duba, ba ina rokon mukami ba.
Tattaunawar ta ‘yan jarida na zuwa ne kasa da sa’o’i 24 da Wike tare da tsohon gwamnan jihar Ebonyi, Dave Umahi da Sanata Godswill Akpabio tare da Tinubu suka saki labule a fadar Aso Villa.
A Wani Labarin Kuma, Kwankwaso Ya Yi Magana Akan Tsohon Sarkin Kano
Tsohon gwamnan jihar Kano Rabi’u Musa Kwankwaso ya mika sakon ta’aziyya da godiyarsa ga marigayi Sarkin Kano Ado Bayero ya wanda ya rasu
a watan Yunin 2014.
Sarkin wand guda ne cikin shugbannin addinin musulinci da ake girmamawa, kuma mai sukar mayakan Boko Haram.