By Abbas Yakubu Yaura
Kungiyar malaman jami’o’i ta dage matakin datayi niyyar dauka na sake tsunduma yajin aikin, inda tace ana ci gaba da tuntubar juna.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar bayan taron majalisar zartarwa na kasa.
Taron wanda aka gudanar a Sakatariyar kungiyar ta kasa Festus Iyayi dake Jami’ar Abuja, a ranar Asabar, 18 ga watan Disamba, 2021, domin duba matakin aiwatar da yarjejeniyar aiki ta gwamnatin tarayya da ASUU ta ranar 23 ga Disamba, 2020 da sauran batutuwa masu alaka hakan.
A cikin wata sanarwa mai taken “Cin Fuskar Ya isa haka” mai dauke da sa hannun shugaban ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke, malaman sun nuna damuwar su kan yadda Gwamnatin Tarayya ta juya baya ga shirin kafa kwamitin cikin gida domin duba daftarin da aka amince da shi yayin tattaunawa tsakanin bangarorin biyu, a shekarar 2009.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa tun da farko dai ASUU ta bayyana shirin shiga yajin aikin saboda gazawar gwamnatin tarayya wajen biyan bukatun ta.
Baya ga kudaden alawus-alawus na ma’aikata, ASUU tace bukatunta sun hada da sake duba dokar NUC don dakile yaduwar jami’o’in da gwamnatocin jihohi basa ba da kudaden da ake dasu, da kuma Amincewa da Maganganun Bayar da Bayani na Jami’ar (UTAS) tare da dakatar da tsarin (IPPIS) da kuma murdiya cikin biyan albashi.
Sauran kuma su ne sakin kudaden da aka tara na karin girma, da kuma bita da rattaba hannu kan daftarin aiki na sake tattaunawa na shekarar 2009 tsakanin ASUU da gwamnatin tarayya.
“ASUU tace ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen neman a inganta jindadin su da kuma yanayin hidimar mambobinmu. Duk da haka, za mu yi tir da duk wani yunƙuri na lalata ƙungiyar tare da dakile fafutukarmu ta kishin ƙasa don samar da ingantaccen tsarin jami’a ta hanyar yada farfaganda a hukumance da aka kafa bisa la’akari da raba gardama.
“Duk da haka, idan akayi la’akari da kokarin shiga tsakani da tuntubar da ake yi, NEC ta yanke shawarar sake duba lamarin nan gaba da nufin yanke hukunci kan mataki na gaba.”