A ranar Juma’a ne bayan da gwamna Obaseki na jihar Edo bai samu damar tsayawa zaben fidda gwani da za a yi a jihar Edo ba karkashin inuwar Jam’iyyar APC, Tsohon Mataimakin Shugaban kasar nan Alhaji Atiku Abubakar ya kira gwamnan tare da masa tallar Jam’iyyar PDP.
Tsohon Mataimakin Shugaban kasar, wanda kuma yayi takarar shugabancin kasar nan a jam’iyyar PDP a zaben shekara ta 2019, ya nuna sha’awarsa na ganin Obaseki ya dawo Jam’iyyar tasa ta PDP.
Sai dai kundin tsarin shugabancin Jam’iyyar PDP ya tsara duk wanda zai yi takarar wani shugabanci a jam’iyyar dole ne ya zama yayi rijista da Jam’iyyar watanni 18 kafin yin zabe.
Wata majiyarmu ta bayyana cewa Atiku yana tattaunawa da wasu gwamnonin PDP don ganin an jawo ra’ayin Obaseki ya dawo Jam’iyyar.
A wani ci gaba kuwa, shugaban kwamitin tantancewa na Jam’iyyar APC na jihar Edo Jonathan Ayuba ya bayyana cewa, Jam’iyyar APC ta hana shi damar shiga zaben ne bayan da aka same shi da badakala game da takardun karatunsa.
Wasu masana siyasa na ganin cewa gwamna Obaseki zai iya komawa Jam’iyyar PDP ganin yadda abubuwa suka yi tsami tsakanin gwamnan da kuma shugana Jam’iyyar APC na kasa Adams Oshiomhole.