Rahotannin da ke shigowa Dimokuradiyya na nuni da cewa; sabon shugaban riƙo na jam’iyyar APC Victor Giadom ya soke zaɓen fidda gwani na gwamnan jihar Edo.
Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa Victor Giadom na cewa ya dauki matakin ne bisa umarnin da kotu ta bayar a baya wanda ya ba shi damar yin hakan.
A cewarsa, ya samu goyon bayan membobin kwamitin Gudanarwa na Jam’iyyar.