Shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya, kuma gwamnan jihar Ekiti, Fayemi ya tabbatar da cewa; babu wata hujja dake nuni da cewa; gwamnan jihar Ribas, Wike ya rusa masallaci a Fatakwal kamar yadda ake yadawa. Fayemi ya bayyana hakan ne a yayin da ya kai ziyarar gani da ido a jihar inda ya ziyarci wurin da ake cewa Gwamna Wike ya rushe Masallacin a titin Biambo dake School road a Rainbow Estate a karamar hukumar Obio/Akpor a jihar Ribas.
Gwamna Fayemi ya nemi Gwamna Wike da ya bai wa Musulmi dama a duk lokacin da suka bukaci wani wuri da za su gina masallaci. Gwamna Fayemi ya ce; a dai abin da ya gani babu wata hujjar cewa an taba ginin masallaci a wurin, balle a ce an rushes hi. Ya ce; daga abin da ya gani sashen gini ne kawai. Ya ce; babu komai a wurin da har zai kawo irin wadannan musayar kalamai da ake yi kafafen watsa labarai.
Wike ya dai zagaya da Gwamna Fayemi wurin da aka ce ya rushe Masallacin, inda ya yi kira ga al’umma da su guji yada labaran da zai kawo rikicin addini domin a cewarsa dukkanin addinai Allah guda suke bautawa. Inda yace; yanzu gas hi shugaban gwamnoni ya tabbatar da cewa babu wani masallaci a wurin.
Wike ya ce ya yi mamaki yadda ake ta yamadidi da shi cewa ya rusa masallaci. Ya ce; babu yadda za a yi ya ga masallaci sai kuma ya ba da umurnin a rusa masallacin.