Kungiyar kiristocin Nijeriya wato CAN a takaice ta gargadi gwamnatin tarayya da ta tabbata ta yi watsi da shirin nan na killace Fulani makiyaya a wuri daya wato shirin RUGA kamar yadda aka fi saninsa da shi.
Shugaban kungiyar Kiristocin, Samson Ayokunle, ya bayyana cewa kungiyar a kasarnan ba ta amince da wannan shiri ba kuma tana gargadin gwamnatin tarayya ka da ta kuskura ta ci gaba da wannan shiri.
Idan ba a manta ba a watan Mayu ne gwamnatin tarayya ta kaddamar da wannan shiri na RUGA. Sai dai kuma tun bayan bayyana wannan kudiri na ta aka rika caccakar gwamnatin game da wannan tsari da take so ta yi wa Fulani Makiyaya. Wannan kalubalen ya fi fitowa ne musamman daga mazauna yankunan kudancin Nijeriya, duk sun tsoki lamirin gwamnati akan wannan shiri. Daga baya dai gwamnatin tarayya ta bayyana dakatar da shirin.
Kungiyar CAN ta ce gaba daya kiristocin Njeriya ba su tare da wannan shiri kuma ba za su goya wa gwamnati baya ba game da shi. Ya kuma tabbatar da cewa; sauran limaman coci-coci da suka halarci taron kungiyar sun bayyana cewa kiristocin kasarnan na daure tamau wuri daya kuma gaba dayan su suna tare a matsayi guda game da shirin RUGA a kasarnan.
Sai dai kuma wasu jihohi kamar su Zamfara da Kano, tuni har sun fara share filaye domin kaddamar da shirin a jihohin su. A jihar Zamfara, gwamnan jihar Dk. Bello Matawalle, ya ce za a gina wannan alkarya na Fulani tare da gina asibitoci, makarantu da kasuwanni domin jin dadin makiyayan.
Matawalle ya ce zai kaddamar da gina wannan alkarya ne a ranar da za a yi bukin cikan gwamnatinsa kwanaki 100.