A ranar Litinin din da ta gabata ne mazauna garin Masaka da ke karamar hukumar Karu ta jihar Nasarawa suka shiga cikin firgici bayan da dan wani mutum na farko mai suna Tunde Badejo ya daba wa mahaifinsa Badejo Idowu wuka da tayi sanadiyar mutuwar sa har lahira, bisa zargin mallakar wani filin gado.
Jaridar City & Crime ta samu labarin cewa Tunde ya shafe sama da shekara guda yana cin zarafin mahaifinsa.
A lokacin da wakilin Jaridar Daiky Trust ya ziyarci wurin, matar marigayin Madam Tolani Badejo, ta ce mijinta ya nemi Tunde da ya ba shi lokaci domin ya raba fili cikin adalci tsakanin shi da sauran ‘yan uwasa.
Ta bayyana cewa, “Ya kasance a wuyan mijina don filin tun bara. Don haka a gardamarsu ta karshe a ranar Litinin, ya zaro wuka ya daba wa mahaifinsa sau da yawa a kai, wuya, kirji, hannaye da kafafuwansa wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa. Inda na daga murya sai ya gudu.”
KARANTA WANNAN LABARIN: Rundunar Sojojin Najeriya Ta Sake Ceto Wasu ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Dan marigayin na biyu, Ayomide Badejo, ya ce an kai rahoton lamarin ga ‘yan sanda yayin da aka ajiye gawar mahaifinsa a dakin ajiyar gawa.
A wani labarin kuma na daban.
Abun Fashewa Ya Tarwatse, Ya Hallaka Tubabban Yan ta’adda 8 A Bama
Kimanin tubabbun ‘yan ta’addan Boko Haram guda takwas ne suka rasa rayukansu, daya kuma ya jikkata yayin da wani abun fashewa (IED), ya tarwatse a wani wurin zubar da shara da ke karamar hukumar Bama ta jihar Borno a ranar Litinin, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
An samu labarin cewa tsaffin ‘yan ta’addan na daga cikin mutane 800 da aka dawo da su garin Bama kwanan nan inda aka tsugunar da su a makarantar Sakandaren ’yan mata ta gwamnati da ke Bama.
Kafin faruwar lamarin Tubabbun ‘yan ta’addan da aka ce sun fito ne daga garin Bama da laifin yin mu’amala da wasu ’yan ta’addan na Boko Haram a wata kasuwa da ake kira “Daula” da ke wajen kauyen Goniri a garin Bama.
Zagazola Makama, wani kwararre a fannin yaki da yan tada kayar baya a tafkin Chadi, ya ce tsaffin ‘yan ta’addan sun karbi tarkacen daga hannun tsoffin abokan aikinsu (Boko Haram), wadanda har yanzu suke buya a dajin Sambisa ba tare da sanin cewa wasu daga cikin kayayyakin sun hada da wani bam da bai tashi ba. wanda aka yi watsi da shi bayan harin da sojoji suka kai.
Majiyar ta ci gaba da cewa, ciniki tsakanin tsoffin ‘yan Boko Haram da abokan aikinsu na baya ba wani sabon abu ba ne, inda ta ce a lokuta da dama idan suka ba su tarkace sai su rika musayar kayan abinci, kamar masara, gishiri, da Maggi da sauran su. -kayan masarufi kamar su tufafi, fetur da magunguna.
“Bayan sun karbi kayayyakin, za su zauna a bayan garin Bama don warwaresu su kafin su shigo da su cikin garin don sayar wa wakilansu. Suna cikin aikin warwarewar ne sai wani bam din ya tashi, inda nan take suka kashe takwas daga cikinsu yayin da daya daga cikinsu ya tsira da raunuka.