Kotun Kenya ta amince da dokar haramta luwadi, Inda Manyan Alkalan Kotun da ke Nairobi suka amince da dokar haramta madigo da luwadi a Kenya nan take.
Babbar Kotun Kenya ta ki soke dokar da ke haramta luwadi da madigo a kasar, matakin da ake kallo a matsayin gagarumin koma-baya ga masu wannan dabi’ar.
Kungiyoyin Kare Hakkin ‘Yan Luwadi da suka shigar da kara shekaru uku da suka gabata a gaban kotun, sun yi fatan cewa, kasar ta kenya za ta bi sahun kasashe irinsu Angola da India wajen kawo karshen dokar haramta luwadin.
Sai dai Kotun ta ce, dokar haramcin bata saba wa kundin tsarin mulkin kasar ba, yayinda ta yi la’akari da al’adun gargajiyar da kasar ta gada.
Jim kadan da yanke wannan hukuncin, masu luwadi da madigo suka fashe da kuka a harabar kotun, tare da rungumar juna da kuma sharewa juna hawaye.