Daga Bello Abubakar
A cikin wata takarda da Jamíyyar ta fitar a jiya jim kadan bayan jawabin Shugaba Muhammad Buhari ta hannun Sakatarenta na kasa Kola Olagnondiyan, ta ce babu komai a cikin jawabin Baba Buharin sai tsantsan karya da fadin abin da ba a yi ba, kuma ba za a iya yi ba.
Takardar ta ce ”Jawabin Buhari babu wani fata ga bayin Allah da ake kaiwa hare-hare, satar jamaá, fadace-fadace da zubar da jini da ke faruwa a wasu sassan kasar nan”.
”Abin takaici ne a ranar da aka kira ta Demokradiyya, kawai sai Shugaban kasa ya kaikaice ya yi ta jawabi yana sharara karya, maimakon ya fuskanci batutuwan lalacewar tattalin arziki da bakin talauci, wadanda suka zama sanadin ficewar ýan kasa zuwa kasashen waje domin ayyukan bauta”
Takardar ta cigaba da cewa ”Yaushe ne Gwamnatin da ke da kashi a cikin wandonta na cin mutuncin demokradiyya, magudin zabe, rufe gidajen yada labarai, cin zarafin abokanen adawa, take hakkin fadin albarkacin baki, cin mutuncin jama’a da tsare bayin Allah ba tare da wani dalili ba, har za ta yi maganar wata demokradiyya. Hakika duk wadannan bayanai suna nan, har ma a ofisoshin jakadanci irin na kasar Amurka”
Takardar ta kara da cewa ”Abin takaici ne, irin zaluncin da aka yiwa Abiola har ta kai ga sanadin mutuwarsa da samar da ranar 12 ga watan June, to Buhari na yin abin da ya fi haka a yanzu, ta hanyar mulkin kama-karya na jamíyyar APC.
Takardar ta kammala da cewa ”Yau din nan 12 ga watan June, duk daya take da ranar 23 ga watan Fabrairu 2019, ranar da aka yi aringizon zabe.
An take mana hakkinmu, kuma babu shakka, dan takararmu Atiku Abubakar na cigaba da neman hakkinsa, Inji shi