Malam Garba Shehu, mai magana da yawun Shugaban kasan Nijeriya, Shugaba Muhammadu Buhari ya karyata labaran da suke yawo a kafafen yada labarai cewa akwai takun saka tsakanin shugaban kasan da mataimakinshi, Farfesa Yemi Osinbajo. Ya bayyana labaran a matsayin karya ne a wata takardar manema labarai ne da ya fitar a ranar Jumma’a.
“Idan aka lura za a fahimci cewa da yawan wadanda aka tafi dasu a baya, ba a basu mukamai a bana ba a ofishin shugaban kasa. Cikin yiwa shugaba Buhari biyayya ne, mataimakin nashi ya rage wasu hadiman nasa a kan wannan dalili ne.
“Dalilin yin hakan kuwa shi ne tsare kudaden ‘yan kasa daga almubazzaranci.
“Da haka ne muke tabbatar muku da cewa babu wata takun saka tsakanin Shugaba Muhammadu Buhari da mataimakinsa, Yemi Osinbajo. Har yanzu babu komai tsakaninsu face aminci kuma da haka za su bar tarihi ga na baya.
“Labaran da suke fitowa na cewa akwai tsama tsakanin shugabannin yana fitowa ne daga wasu bakuna da basa son su ji alheri daga fadar gwamnati. Sai suke fakewa da rage ma’aikatan suna shirya tatsuniyoyinsu.
“An dade ana tankade da rairayan ma’aikatan fadar gwamnati. Kuma hadiman shugaban kasa basu kai na mataimakinshi yawa ba. Rage su kuma ba wai don cin zarafin ofishin mataimakin shugaban kasar bane kamar yadda kafafen yada labarai suke ta yadawa.
“Babu wanda ya kai shugaban kasar ikon da gwamnati. Kafafen yada labara su daina nuna wa kamar wasu ne suke rike da gwamnatin. Babu wanda zai kai shugaban kasa karfin da har zai bashi umurni”, a cewar Garba Shehu.