• Babu gaskiya a labarin da ke cewa an gayyaci Sheikh Abubakar Gumi.
• Ina shiga daji ne da tallafin gwamnati da kuma jami’an tsaro.
• Banyi Laifin komai ba, ta ya za a kama ni?.
Shahararren malamain addinin Musulunci nan dake jihar Kaduna, wato Sheikh Ahmed Gumi, ya karyata rahoton da ake ya dawa cewa, hukumar tsaro ta farin kaya wato DSS ta gaiyace shi ofishinta, domin amsa wasu tabbayoyi kan bayanan kushe, da yayi kan rundunar soji ta kasa.
Lokacin da ya ke zantawa da kafar ya da labarai ta Channels, bayan idar da sallar juma’a da ya jagoran ta a masallacin Sultan Bello dake Kaduna, Sheikh Gumi ya ce, dukkannin shiga dazukan da ya keyi, domin tattaunawa da yan bindiga, da tallafin gwamnati, da kuma hukumomin tsaro a ciki, don haka Bai aikata laifin komai ba.
Inda ya ce” Babu wanda ya gayyace ni, domin amsa wasu tambayoyi, ko kama ni,”inji Sheik Gumi.
KARANTA WANNAN LABARIN: Jan hankali kan Masu yabo kan kalaman da Basu dace ba
Ya Kuma Kara da cewa, “Tun da na fara shiga daji, Ina shigane tare da isasshen tsaro, wanda da sanin jami’an yan sanda, hukumar DSS, Sarakunan Gargajiya, da kuma shuwagabannin Fulani, Wanda banta ba shiga ni kadai ba.” Inji shi.