Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum a ranar Alhamis din da ta gabata yayi ziyarar bazata ga wasu cibiyoyin kula da lafiya na gwamnati ba tare da sanar da su ba, inda ya tarar da wasu jami’ai na karbar Naira 8,000 zuwa N10,000 daga hannun majiyyata, yayin da aka samar da shirin kula da lafiyar kyauta.
Zulum ya gayyaci Kwamishinan Lafiya na Jihar, Misis Juliana Bitrus, kuma ya nemi ta bi shi domin zagayen da kuma ganewa idonsu, a cikin motar bas mai kujeru 10 da aka saba amfani da ita don ayyukan filin jirgin sama. Gwamnan ya bar gidan gwamnati da misalin karfe 1:30 na rana ba tare da wani ayarin motoci ba kuma babu jiniya, lamarin da ya baiwa kowa mamaki da mamaki. Kuma hatta ita kwamishinar Lafiya bata san shirin Gwamnan ba.
An kashe wani Mai Garkuwa Da mutane yayin karbar kudin Fansa
Zulum ya garzaya kai tsaye zuwa sabuwar cibiyar kiwon lafiya ta matakin farko da aka kafa tare da cikakkun kayan aiki da ke unguwar Gwange II a Maiduguri inda ya gano cewa wasu ma’aikata na karbar Naira 8,000 zuwa Naira 10,000 kafin a tantance tare da kula da masu fama da cutuka irin na zazzabin cizon sauro.
Gwamnan ya umurci hukumar kula da lafiya matakin farko ta jihar Borno da ta yi cikakken bincike, domin gano duk masu laifin tare da daukar matakin ladabtarwa.
Zulum ya kuma yi bakin cikin ganin cewa wannan cibiyar kiwon lafiya ta matakin farko tana da ma’aikatan lafiya guda daya kacal da za su rika kula da marasa lafiya, duk da cewa akwai ma’aikatan lafiya 29 da ke kan albashin Gwamnati.
Gwamnan ya zarce irin wannan cibiyar kula da lafiya ta matakin farko da ke Gwange I, amma hakan ya ji dadi.
Zulum ya iske ma’aikatan lafiya a kasa suna kula da marasa lafiya ba tare da an kyare su ba.
Gwamnan yayi farin ciki kuma ya yabawa ma’aikatan da suka kasance mutanen kirki.