Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Alhaji Abdulkadir Balarabe Musa yace wahala da tsadar rayuwa da ake ciki yanzu da Buhari ke mulkin kasar nan yafi na lokacin Jonathan.
Balarabe Musa yace maganar gaskiya Buhari da Jam’iyyar APC sun cuci kasar nan, ba abunda suka tsinana a kasar nan se karya da surutan banza.
Abdulkadir ya bayyana haka ne a yayin da yake zantawa da manema labaru a hutun karshen makon daya gabata,yace kamata yayi a fatattaki Buhari da Jam’iyyar sa ta APC a kasar nan.
Maganar gaskiya Jonathan yafi Buhari taka rawar gani a kasar nan, duk da irin abunda ya faru lokacin Jonathan yafi Buhari.