• Barayin waya sun farmaki wasu yan kasuwa a garin Lokaja.
• Mutun biyu sun mutu sanadiyar harin, ya yin da wasu kuma suka sami raunuka.
• Kwamishinan yan sandan jihar Kogi ya tabbatar da afkuwar lamarin kamar yadda Mai magana da yawun rundunar ya bayyana.
A kalla mutane biyu ne suka mutu a wani farmaki da ake zargin barayin waya sun kai a yankin Felele na Lakoja, babban birnin jihar Kogi.
Rahotanni sun bayyana cewa, an sari wani dan kasuwa ya yin farmaki, lokacin da daya daga cikin barayin ya kwace wayar hannun sa.
Wani shaidan gani da Ido, ya bayyana wa jaridar Daily Trust cewa, Maharan sun kashe wani dan kasuwa.
Kazalika shaidan ya ce, “barayin sun kuma kashe wani mutun kuma suka kona gawar shi, ya yin da wasu suka sami raunuka, amma an kai su asibiti domin kula da lafiyar su” inji shi.
Ko da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan jihar ta Kogi DSP Williams Aya, ya tabbatar da afkuwar lamarin inda ya ce rundunar ta sami kiran gaggawa daga al’umar yanki, da musalin karfe 10 na safen ranar litinin din da ta gabata.
Jami’in ya kuma ce, rundunar ta kama wadanda ake zargi da kai farmakin, Wanda akwai wani mai suna Muhammed Mubarak, da Sulaiman Yakubu wadanda yan kungiyar asiri ne da ake Kira da Aro Berger” inji shi.
A karshe ya ce, ana cigaba da gudanar da bincike kan lamarin kamar yadda kwamishinan yan sandan jihar ya umarci sashin binciken manyan laifuka na jihar.
Comments 1