Wakilinmu Shu’aibu Ibrahim Gusau
Kwamitin karbar mulki karkashin jagorancin tsohon mataimakin gwamna, Mal. Ibrahim Muhammad Wakkala, ta bayyana cewa abinda kwamitin Mika mulki ta basu a matsayin bashin da ake bin gwamnatin da ta gabata ya Kai sama da Naira biliyan Dari biyu da hamsin da daya.
Wakkala, ya bayyana haka ne lokacin da yake yiwa manema labaru bayani a gidan gwamnati, ya ce kwamitinsu Yana nan Yana gudanar da aikinsa.
Ya Kara da cewa wannan addadi na bashi shine suka karba daga kwamitin gwamnatin Yari, hakan yasa Suma sun kafa kwamitoci, wadanda zasubi ma’aikatun gwamnati don binciko gaskiyar al’amari.
Tsohon Mataimakin gwamnan Malam Ibrahim Wakkala, ya Kara da cewa zasuyi aikinsu tsakani da Allah ba domin suci mutuncin wasu ko wani ba, zasuyi aikinsu ne don taimakon al’ummar jihar zamfara.
Shugaban kwamitin ya Kara da cewa matukar suka ga akwai bukatar su gayyato tsohon gwamna Abdul’aziz Yari Abubakar, to zasu gayyatoshi su zauna dashi domin yazo ya warware masu zare da abawa na wannan bashi, batare da shakka ko tsoro ba.