Wata mai jego mai suna Maryam Bilal da madaurin aurenta Musa Khalil sun gurfana a gaban kotun Majistare mai lamba 62, dake zaman ta a garin Minjibir, karkashin mai Shari’ah Ibrahim Sarki Ibrahim, bisa tuhumar hada kai da aikata laifi da kuma cutarwa.
Laifukan dai sun saba da sashe na 97 da 322 na kundin tafi da shari’ar Musulunci na jihar Kano.
Wani mutum mai suna Aminu Ibrahim ne ya yi karar su a ofishin ‘yan sanda na Minjibir cewar Musa Khalil din ya aura masa Maryam alhalin tana dauke da juna biyu, kuma watan ta hudu da kwana ashirin da takwas ta haihu.
Ko da Dan sanda mai gabatar da kara Sajan Kabiru Bashir ya karanta musu kunshin tuhumar da ake musu, sai suka musunta. A nan ne mai Shari’ah Ibrahim Sarki Ibrahim, ya daga zaman zuwa ranar 14 ga wannan watan da mu ke ciki domin ci gaba da sauraren shari’ar.
Daga nan ne Lauyan da yake kare su ya roki kotun da ta ba da belinsu. Kotun ta amince bisa sharadin mutane biyu masu kamala su tsaya musu sannan kuma su bada hotunan su na passport guda biyu a kotun sannan kuma dan sandan kotun ya je ya gano gidajen su.
In kuma wadanda akai belin suka tserewa shari’ah masu belin za su bada duba dari dari. Shafin Al’ummata sun labarto cewa; bayan an fito daga kotun Maryam din ta shaidawa wakilinmu Abubakar sabo cewa wani ne mai suna Sunusi Bala alale ya yi mata.