Matar gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa wato Edith ta kamu da cutar korona, kamar yadda Sakataren watsa labaran gwamnan, Olisa Ifeajika ya tabbatar.
Ifeajika ya bayyana hakan ne a garin Asaba a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, inda ya ce hakan ya faru ne bayan gwajin da aka yi wa gwamnan da matarsa kwanaki kadan da kammala killace kansu da suka yi.
Gwamnan da matarsa sun killace kansu ne bayan da aka samu ‘yarsu da cutar a makon da ya gabata. A cewarsa, dukkansu matar da ‘yar ana ci gaba da duba lafiyarsu a inda aka killace su.
Gwamnan ya mika godiyarsa ga al’ummar Delta bisa addu’ar da suka rika yi musu, inda ya bukaci da su ci gaba da yi musu addu’a.
Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatinsa ba za ta yi kasa a guiwa ba wajen yaki da annobar korona, inda ya shawarci al’umma da su bai wa gwamnatin jihar hadin kai tare da bin ka’idojin da NCDC suka fitar na dakile yaduwar cutar korona.