Awanni kadan bayan Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya ziyarci tsohon Gwamnan Kano Ibrahim Shekarau, an hangi fuskar wata tawaga daga gida Rabi’u Musa Kwankwaso, itama ta isa Gidan Shekarau din dake Mundubawa.
Baki daya bangarorin sunje ne domin ganin yadda zasu Mallaki Shekarau din, domin zama da su ko dai APC, ko kuma a NNPP.
Daga gidan Kwankwaso wata tawaga ta musamman ya tasa domin dai saduwa da Shekarau, da nufin tattaunawa da shi kan shirin sa na komawa jami’iyyar NNPP.
Tuni dai ake hasashen cewa Shekarau din zai koma jam’iyyar NNPP, wadda Dakta Rabi’u Kwankwaso ke a matsayin jagoranta, biyo bayan zargin ƙin yi masa adalci a jam’iyyar APC karkashin Gwamna Abdullahi Ganduje.
Tuni dai aka jiyo Kwankwason na bayyana cewa kofar su a bude take domin karbar Bakuncin Sanatan Kano tsakiya.
Baki daya dai mutanan biyu wato Shekarau da Kwankwaso a Jiya da daddare suka sauka a jihar Kano, bayan da suka dawo daga Abuja.