A daren yau Lahadi kungiyar Bayern Munich za ta kara da PSG a wasan karshe na cin kofin zakarun nahiyar Turai da zai gudana a birnin Lisbon na kasar Portugal.
Kungiyar Bayern Munich ta lashe wannan kofi har sau 5, yayin da PSG ba ta taba samun nasarar lashe shi ba.
Kungiyar Munich na gadara da fitattun ‘yan wasan ta irin su Robert Lewandowski da ake yiwa lakabi da ‘dodan raga’ da Muller da Alaba da sauran su.
A yayin da kuma PSG ke tinkaho da matasan ‘yan wasa irin su Neymer da Kylian Mbappe da Angel Di Maria da Icadi wadanda suka taka gagarumar rawa wajen ganin kungiyar ta samu nasarar zuwa wannan matsayi.