Amurka ta yi alkawarin ba da taimakon kudi don tabbatar da ingantacciyar hanyar samun lafiya a yankin Falasdinu a ranar Juma’ar nan, yayin da shugaban Amurka Joe Biden ya ziyarci yankin a ziyarar da yake yi a yankin Gabas ta Tsakiya.
Da ya ziyarci asibitin Augusta Victoria da ke Gabashin Kudus, Biden ya yi alkawarin ba da taimakon kudi dala miliyan 100 ga wata kungiyar asibitocin yankin.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa Kudin, wanda za a raba tsakanin wurare shida, na bukatar amincewar majalisar dokokin Amurka.
Biden ya yi niyyar ba da sanarwar tallafin dalar Amurka miliyan 316 a ziyarar da ya kai ranar Juma’a a Yammacin Kogin Jordan, a cewar wani jami’in Amurka.
An kuma shirya zai gana da shugaban Falasdinawa Mahmoud Abbas.
Biden na ziyararsa ta farko zuwa yankin Gabas ta Tsakiya a matsayin shugaban kasar Amurka.
A ranar Juma’ar nan ne aka shirya zai wuce kasar Saudiyya a cigaba da ziyarar da yake yi. (dpa/NAN)