Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) reshen jihar Kebbi, ta tura jami’anta domin kula da cunkoson ababen hawa a lokacin bikin babbar Sallah a jihar.
Kwamandan sashin, hukumar kiyaye hadurra ta tarayya, shiyyar jihar, CC Yusuf Aliyu Haruna Kiru ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar Laraba.
Yayin da yake kira ga jama’a da su guji duk wata dabi’a ta rashin da’a da ka iya jawo hatsarin ababen hawa, Yusuf , ya shawarci direbobi da su guji gudun wuce gona da iri, tukin ganganci, Lodi fiye da kima, yin amfani da waya lokacin tuki akan tituna, da Kuma yin tuki alhalin matukin na cikin maye.
Ya ce rundunar ta hadin gwiwa da dukkan hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki domin ganin an gudanar da bukukuwan Sallah ba tare da samun wata matsala ba a fadin jihar.
Sai dai Yusuf ya bukaci direbobi ‘yan kasuwa da su sanya na’urar da ke hana saurin gudu a cikin motocinsu domin kiyaye ka’idojin da aka ba da shawara akai cikin ababen hawa don samun tsira.
Ya Kuma Kara da cewa a hali na gaggawa ai kokarin Kiran wannan lambar Kai tsaye ta 122 a kyauta.
A wnai labarin kuma na daban
Cibiyar ‘yan jarida ta kasa da kasa (IPC), ta kammala horar da zababbun ‘yan jarida na kwana biyu kan inganta kariya da tsaro a Kano.
Cibiyar, ta ce an tsara horon ne don inganta lafiya baki ɗaya, tsaro na zamani da kuma yadda ake tafiyar da ƴan jarida a kashin kansu a lokutan da suka sami rauni yayin da suke kan aiki.
Horarwar na inganta iya aiki, wanda ya gudana a Otal din Chilla Suites, ya jawo hankalin ‘yan jarida sama da 25 daga gidajen jaridu, jaridun intanet, da kuma yada labarai a jihar.
Da yake kaddamar da horon, Babban Darakta na cibiyar IPC, Mista Lanre Arongundade, ya ce horon na inganta iya aiki ya zama dole dangane da karuwar barazanar ‘yancin ‘yan jarida da tsaro a kasar.
A cewarsa taron bitar na neman kara kwarin gwiwar kwararrun kafafen yada labarai kan matakai da hanyoyin tabbatar da kariya da tsaro, musamman a lokacin gudanar da rahotannin bincike, da kuma bayar da rahotannin ayyuka masu hadari da rahotannin rikice-rikice.
Shugaban Sashen yada labarai da Nazarin kafafen yada labarai na Jami’ar Bayero Kano Dr. Nura Ibrahim wanda ya gabatar da kasida mai taken “Batutuwa masu alaka da bayanan tsaro na zamani ‘Data da Digital Security in Investigative Reporting and Coverage of Dangerous Assignments” ya yi nuni da cewa ‘yan jarida na bukatar sanin dokoki da dama da kuma sanin makamar aiki. tanade-tanade na shari’a, domin zai taimaka wajen kauce wa tarzoma wajen sauke nauyin da ke kansu.
Masanin harkokin yada labarai ya sake jaddada bukatar ‘yan jaridu da ke gudanar da ayyuka masu haɗari don kiyaye bayanan sirri da hotuna daga kafofin yada labarun yayin da suke bunkasa ingantaccen tsaro na zamani.
Ya kara da cewa tsaron tattalin arziki, tsaro na shari’a, tsaro na aiki, da tsaro na jiki, da dai sauransu, sune muhimman abubuwan da ke tabbatar da kariya da tsaro ga ‘yan jaridu masu bincike.
A nata jawabin, Dakta Rukayyah Aliyu Bello, ta ce aikin jarida na bincike aiki ne mai hadari da ke da alaka da kai hare-hare da kisa inda ta kara da cewa idan ‘yan jaridu suka zurfafa a cikin rahotannin su, sai sun yi taka-tsan-tsan da tsaron lafiyarsu fiye da aikin.
Ta ce a lokacin gudanar da rahoton bincike dole ‘yan jaridu su canza kuma su gudanar da bincike tare da samun nasarar aiki sannan kuma ‘yan jaridu su kasance masu lura da tsaro da kiyaye tsaro tare da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.
A lokacin da ake ba da rahotannin rikice-rikice wanda ke zama rahoto mai haɗari ga ‘yan jarida, ta ce dole ne a ba da kulawa sosai saboda yana ɗaukar kyamara a matsayin makaminsa kawai.
Cibiyar Yada Labarai ta kasa da kasa (IPC) ce ta shirya taron tare da tallafi daga gidauniyar MacArthur, Shehu Yar’adua Foundation, Luminate, Ford Foundation, da OSIWA, kan hanyoyin tabbatar da kariya da tsaro a cikin rahoton bincike da bayar da rahoto kan rikice-rikice ko ayyuka masu hadari.